Rundunar yan sandan jihar Nasarawa ta ta ce ta cafke wasu mutane takwas da ake zargi yan fashi da makami ne da ke addabar mazauna karamar hukumar Keffi ta jihar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sanda a jihar, ASP Ramhan Nansel ne ya bayyana hakan, a wata hira ta musamman da manema labarai sukayi da shi garin Lafia, babban birnin jihar, a jiya Lahadi.
Ya ce ankama wadanda ake zargin ne tare da jagoran su Mai suna Shamsu Usman, wanda shine ake zargin ya jagoranci farmakan wani gida a unguwar Angwan Jarmi na karamar hukumar Keffi a jihar Nasarawa.
KARANTA WANNAN LABARIN: Abun da yasa ba’a gani na a Fim, inji Musa Maisana’a
Kazalika ya ce, jami’an rundunar yan sandan sun kuma cafke wasu mutane uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, wadanda ake zargin sun sace matar wani Mai suna Alhaji Ibrahim Sarkinnana a kauyen Ayongo da ke karamar hukumar Awe ta jihar.
A wani labarin Kuma na daban.
Ma’aikatan banki a Ijebu-Ode da kewayenta a jihar Ogun sun yi arangama da rundunar ‘yan sanda kan ikirarin barazanar fashi da makami a yankin.
Wasu bankunan da ke Ijebu-Ode sun rufe bankunan tun ranar Talata suna ikirarin ‘yan fashi sun rubuta takardar sanar dasu, da su kasance cikin shiri da tsabar kudi kafin harin nasu.
Rufe cibiyoyin hada hadar kudi ya tilastawa mazauna garin zuwa Sagamu ko Ago-Iwoye don yin hada hadar banki, an gano cewa rundunar ‘yan sandan dake aiki a Ijebu-Ode, wanda ke ba da mafaka a yankin, ya samu matsala kuma duk da haka ba a gyara ba, wanda ya tilasta masu banki cewa zai zama haɗari a garesu don buɗe kasuwanci ba tare da ingantaccen tsaro ba.
Amma mai magana da yawun ‘yan sanda Abimbola Oyeyemi yace rundunar ta ninka jami’an tsaro a Ijebu Ode, yana mai cewa ba a taba kai harin fashi na banki a jihar Ogun ba a cikin shekaru takwas ko tara da suka gabata baya ga wanda aka yi a yankin Agbara a shekarar 2013.
Abimbola a cikin wata sanarwa daya fitar jiya ya ce rufewar da aka yi bata da wata dabara kuma ba ta dace ba, sanarwar tace, “Sun yi ikirarin cewa ‘yan fashi da makami sun rubuta sako don sanar da su cewa za su kawo musu farmaki, amma basu gabatar da wasikar da ake zargi ga ‘yan sanda ba don gudanar da bincike.
“Don haka umurnin na yin gargadin cewa lallai ma’aikatan banki zasu kasance farkon wadanda ake tuhuma idan wani sabon abu a cikin hanyar fashin banki ya faru a yankin, aƙalla don su bayyana hanyoyin da ba su da tushe.
“Kwamishinan ‘yan sandan CP Edward Awolowo Ajogun ya ba da umarnin gudanar da cikakken bincike kan wannan ikirarin na su na samun wasika daga’ yan fashi da makami.”
Comments 2