Jami’ar Jos sun dauki Yan sakai don yin gadin Dalibai
Prof. Sabastian Maimako shugaban jami’ar dake Jos ya bayyana cewar hukumar makarantar ta dauki Yan sakai don gadin daliban wurin karatunsu da wurin kwanansu.
Prof. Maimako ya bayyana haka ne wajan wani biki na cikar sa shekara biyar na shugabancin Makarantar.
KARANTA:-An hallaka wasu Yan bindaga tare da kwace muggan makamai a hannun su
Yace tun da dadewa matsalar tsaro a kasar nan ya zama ruwan dare
Shine yasa na yanke wannan kudiri a lokaci na na tabbatar da kiyayewar Lafiyar duk Wanda ke makaranta sannan da Kare kayan dake cikin makaranta
Lokacin da muka samu labarin shiwogar Yan bindiga yasa mun kullu makaranta har na tsawon sati biyu babu karatu, sannan akece idan har zamu dawo dole sai mun sanya Yan Sakai wadanda zasu taimaka wajan bada tsaro a makarantar.
A yau dai gashi munyi hakan, sannan mai kula da zaman Lafiya ya baiwa Yan sakai tsari yadda zasu gudanar da aikin.
Bada dadewa ba biyu daga cikin Malaman makarantar nan akai garkuwa dasu.
Prof. Grace Ayanbimpe na daya daga cikin wadan da aka sace tare da mijinta.