Rahotanni daga Jihar Legas na nuni da cewa jami’ar Jihar wato UNILAG na duba yiwuwar dakatar sa dalibar jami’ar mai suna Chidinma Ojukwu wacce ta aika da saurayinta mai gabatar da shirye-shirye a talabijin Steve Usifo Ataga har lahira.
Dalibar mai shekara 21 tana tsangayar koyon aikin jarida ne naakarantar inda kuma take aji ukun karshe.
Matakin Jami’ar na dakatar da dalibar ya zo ne daidai lokacin da bayanai suka nuna karara cewa tana da hannu dumu-dumu wajen kisan saurayin nata, wanda kuma aiki ne ja a kama dalibin jami’ar da wani mummunan aika-aika.
Da ma dai jami’ar ba ta ragar wa kowa muddin aka kama shi da hannu cikin wani mugun aiki, inda kuma jami’ar ta ce ba za ta sauya matsayin ta kan dalibar ba lura da irin munin aikin nata da ake zarginta da aikatawa.
Kazalika a hannu guda rundunar yan sandar jihar ta saki mahaifin matashiyar Mista Ojukwu wanda aka kama bisa zargin daurewa yar tasa gindi kan cewa ba ta aikata kisan ba.
An saki Mista Ojukwu ne karkashin sharadin beli wanda wani mai suna Nkechi Mogbo ya tsaya masa, kuma da ma mazaunin unguwar alfarma ce ta Lekki dake Legas din inda nan ne kisan Steve din ya wakana.