Jami’ar tarayya ta Lokoja ta ce ta dauki nauyin mafarauta 60 domin taimakawa wajen tabbatar da tsaro a harabar jami’ar.
Shugaban jami’ar, Farfesa Olayemi Akinwumi ne ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin da yake jawabi a wani taron manema labarai da ya kira a makarantar, inda ya ce Shirin zai fara aiki ne daga yau Litinin 8 ga watan Nuwamba.
Akinwumi ya ce sace ma’aikatan jami’o’in a sassa daban-daban na kasar ne ya sa aka dauki mafarauta aiki yayin da ya ce ba za a bar dalibai su shiga dakunan kwanan su ba har sai jami’ar ta gamsu da matakan tsaro a harabarta.
Ya Kuma ce, “Masu gudanar da wannan cibiya ba za su yi wasa da tsaron dalibai da ma’aikatan jami’ar ba. Mun ga abin da ya faru kwanan nan a wasu manyan makarantun kasar nan inda aka yi garkuwa da Farfesa da ‘ya’yansu a harabar jami’o’in.”
KARANTA WANNAN LABARIN: Zan Iya Lashe Zaben Anambra inji Dan Jam’Iyar PDP
“Mun dauki sama da mafarauta 60 kuma sun tsara wuraren da masu aikata laifuka za su yi amfani da su a matsayin hanyar tserewa kuma za mu toshe wuraren. Har sai mun gamsu da tsaro a nan wurin.”
Shugaban jami’ar ya kara da cewa an kawo mafarautan ne a cikin jirgin ruwa domin kara kaimi ga kokarin ‘yan sanda da jami’an tsaron farin kaya na Najeriya na samar da isasshen tsaro ga ma’aikata da daliban makarantar.
Akinwumi ya kuma bayyana cewa za a ba wa dalibai 804 shaidar digiri da digirin digirgir, yayin da za a ba fitattun jaruman da suka ba da gudunmawa wajen ci gaban Najeriya digirin girmamawa.
Comments 1