Gwamna Abubakar Sani Bello na jihar Niger ya umarci duk masu rike da mukaman siyasa da ke da sha’awar tsayawa takara ko fitowa a matsayin dan takarar da aka amince da su a dukkan matakan jam’iyyar APC Mai Mulki da su ajiye mukaman su.
Sakataren gwamnatin jihar, Ahmed Ibrahim Matane, ya sanar da wannan umarnin a cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Litinin.
Ibrahim ya ce umarnin ya dace da kundin tsarin mulkin APC.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ganduje ya sake Korar Tsohon Kwamishinan sa Mu’azu Magaji
Ya umarci wadanda abin ya shafa da su bi umarnin kamar yadda aka tsara.
A wani labarin Kuma na daban.
A cikin taka rawar gani, aƙalla ‘yan matan makaranta 30 a jihar Katsina sun karɓi matsayin ‘yan majalisa a majalisar dokokin jihar, a ranar Litinin, don yin kira ga gwamnatin jihar data samar da kashi 35 cikin 100 na mata a fannin ilimin jihar.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa taron zaman majalissar wani bangare ne na ayyukan bikin ranar ‘ya ‘ya mata ta duniya (IDGC) ta shekarar 2021 a jihar Katsina.
A Majalisar, daya daga cikin ‘yan matan da suka dauki nauyin kudirin, Hajara Abdu, mai wakiltar mazabar Mashi, tace matakin, idan an amince dashi, an yi shi ne don magance batutuwan da suka shafi yaran a makarantu a fadin jihar.Tace idan aka kara wa mata nade -nade mukamai a bangaren ilimi, hakan zai bunkasa shigar da ‘ya ‘ya mata a makarantu.
A cewarta, wannan zai karfafawa yara mata su zauna dan kammala karatunsu tare da wucewa zuwa manyan makarantun sakandare da manyan makarantu kwalejoji a jihar.Yan matan makarantar 30 da UNICEF ta koyar dasu a baya, tare da hadin gwiwar gwamnatin jihar kan ilimin zamani da kuma jagoranci.
“Gaskiyar magana ita ce, babu kashi ɗaya cikin huɗu na ‘yan matan dake samun shiga cikin canjin ilimi na gaba, ko dai sun faɗi jarabawarsu ko kuma iyayensu sun ji sun isa aure.” Iyaye su daina janye ‘ya ‘yan mata daga makaranta don yin aure”, a cewar Abdullahi.
Ta kara da cewa ranar yara mata ta duniya ita ce dandalin daya dace don wayar da kan jama’a kan kalubalen tattalin arziki, zamantakewa da al’adu da matasa ‘yan Najeriya, musamman’ yan mata matasa da suke fuskanta a kasar.
Abdullahi yace tun da farko an zabo ‘yan matan 30 daga cikin makarantun sakandare na ‘yan mata (G4G) dake kananan hukumomin Ingawa, Kankia, Baure, Rimi da Katsina a jihar, kuma an horar dasu kan ilimin zamani da kuma yadda zasu yi shugabanci nagari.
Comments 1