A jiya ne Gwamnan Jihar Ribas Ezenwo Nyesom Wike ya caccaki jam’iyya mai mulki akan abubuwa da suka faru har ya kai ga sauyawar sheka da gwamnan Jihar Edo Obaseki ya yi daga Jam’iyyar APC zuwa Jam’iyyar adawa ta PDP.
A yayin da yake bada bayanin nasa a taron manema labarai, Gwamnan ya ce duk wani abun da Jam’iyyar ta fada akan kiyaye doka da ka’ida a bayyane, to a aikace su sukan karya wannan ka’ida din.
Ya kara da cewa babu inda aka taba hana Gwamna mai ci tikiti a duk duniya sai a wannan mulkin na APC.