Jam’iyyar APC reshen Jahar Filato na shirin fidda gwani
Shuwagabanin APC na Jahar sun bayyana cewa zasu fara zaben fidda gwani kamin suyi zaben kasiloli a Jahar a ranar 9 ga watan oktoba.
Jaridar pmnews Mr. Chido Dafat sakataren jam’iyyar APC reshen Jahar Filato yace lokacin da yake zantawa da manema labarai zaben zai kama Rana Litini.
KARANTA:- An garkame Dan najeriya kan yima wata yar shekara 13 fyade a Amerika
Chido ya bayyana cewa sun zabi wani kwamiti da zai tabbatar da wakanar zaben ga duk mai bukatar zama kansila ko Shugaban Karamar Hukuma.
Yace duk wadanda basu cika ka’idojin ko ya biyo ta wata hanyar dabata dace ba za’a dakatar dasu.
Ya cigaba da cewa duk wanda kuma ya cika sharudda to tabbas shi zai sami gurbin zama.
Chido ya bayyana cewa za’a zabi wakilan jam’iyyar ne a ranar Laraba 24 ga watan Yuni
Yace salon zaben zai kasance a sirri ne.
Comments 1