Da alama yanzu haka Hukumar Zabe INEC na cikin wani halin tsaka mai wuya, saboda watakila wasu jam’iyyun siyasa a kasar zasu iya yin fito na Fito da ita.
Babban abinda zasu saka hukumar a gaba wajen cimma bai wuce dage lokacin da ta basu ba, domin dai su kammala zaben fidda gwani na yan takarar su, wadanda zasu tsaya musu takara a zaɓen 2023.
Kwamitin bayar da shawarwari ga jam’iyyun, a zaman da suke gudanarwa da INEC din, ya bayar da shawarar kara mako uku, ga jam’iyyun domin samun damar kammala zaben fidda gwanin.
Shugaban kwamitin Eng Yabagi Yusuf Sani, ne ya mika rokon a madadin sauran manbobinsa, inda ya nuna bukatar hukumar INEC ta dage wa’adin 3 ga watan Yuni, domin dai jam’iyyu su samu damar kammala zaben fidda gwanin.
Kazalika, shugaban jam’iyyar ZLP Chief Dan Nwanyanwu ya ce kara wa’adin ne kadai hanyar da zata basu damar kammala aikin gaban su.
A nasa bangaren, shugaban hukumar zaben Farfesa Mahmoud Yakubu, ya ce sun gudanar da taron ne kamar yadda jam’iyyun siyasa suka buƙata.
A cewar sa, dukkan bukatun da shugaban kwamitin ya bayar ya saurara, kuma zasu duba batutuwan sa suka tattauna a zaman da suyi nan gaba, musamman batun karin wa’adin ga jam’iyyun.
Comments 1