Gwamnatin Jigawa ta bai wa hukumar NYSC gine-ginen da ta ginawa masu bautar kasa a dukkanin kananan hukumomi 27 dake jihar, inda Darakta Janar na NYSC din, Birgediya Janar Shuaibu Ibrahim ya karba.
Gwamnan jihar, Alhaji Muhammad Badaru wanda Kwamishinan ilimi, Alhaji Lawal Danzomo, ya wakilce shi a yayin mika gine-ginen a ranar Juma’a a garin Kazaure.
Badaru ya nuna wa Daraktan NYSC din wadansu daga cikin kananan hukumomin wanda suka hada da Dutse, Gwiwa da Kazaure, inda ya duba gine-ginen. A cewarsa, manufar wadannan gine-gine shi ne samar wa da wadanda aka turo jihar bautar kasa nagartattun wuraren kwana.
Gwamnan ya tabbatar da cewa gine-ginen na dauke da dakunan kwana a dukkanin kananan hukumomi 27 dake jihar.
Sannan har wala yau suna dauke da wuraren koyar da sana’o’in dogaro da kai, makarantun Firamare, ofisoshi wanda tsohon Darakta Janar na NYSC din, Manjo Janar Salisu Kazaure ya fara samarwa tare da hadin guiwar kare muradun karni da kuma NYSC din.