Gwamnatin jihar Nasarawa ta fara horar da ma’aikatan kiwon lafiya sama da 300 Jim kadan da zuwan allurar rigakafin a jihar.
Horarwar ma’aikatan kiwon lafiyar ita ce a samar musu da kayan aiki ta yadda za a yi allurar rigakafin cutar ta COVID -19.
Shugaban gudanarwa na Hukumar Kula da Kiwon Lafiya a matakin farko, Dokta Mohammed Adis wanda ya bayyana hakan a wata tattaunawa da ya yi da manema labarai a Lafia, ya ce horon ya yi daidai da sa hannun Hukumar Kula da Kiwon Lafiya a matakin farko wajen kula da COVID – 19.
A cewar Adis, amsar da gwamnati da kuma yarda da mutane ke bayarwa shi ne jihar na da kwarin gwiwa, yana mai bayanin cewa ma’aikatan kiwon lafiyar da za su halarci horon an zabo su ne daga cibiyoyin kula da lafiya na farko da kuma manyan asibitoci a fadin kananan hukumomin 13 na jihar.
Dokta Muhammed Adis ya ce har ila yau “horon ya zama wajibi ne a ma’aikatan kiwon lafiyar yadda za su gudanar da aiwatar da allurar rigakafin.
COVID -19 sabuwar annoba ce kuma allurar rigakafin ta bambanta da allurar gargajiya ta sauran cututtukan da aka sani in ji Adis.
Shugaban kula da lafiya na farko duk da haka ya lura cewa hukumar tana aiki kafada da kafada da Hukumar Lafiya ta Duniya don tabbatar da cewa ma’aikatan sun kasance suna da cikakkun bayanai game da matakan da aka sanya domin gudanar da ingantaccen maganin rigakafin COVID -19 lokacin da suka isa jihar.
A halin da ake ciki, Kwamishinan lafiya na jihar Nasarawa, Pharmarcist Ahmed Yahaya Talata ya koka da yadda ake samun masu tayar da hankali a jihar yana mai cewa kashi talatin cikin dari na asibitocin masu zaman kansu a jihar ko dai ba su da wuraren kiwon lafiya, kwararrun ma’aikata ko suna aiki ba tare da lasisi a ciki ba.