Hukumomin kula da magunguna na jihohin Sokoto da Nasarawa sun rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da masana’antun sarrafa magunguna na cikin gida, a kokarin da ake na samar da kayayyakin kiwon lafiya a cibiyoyin lafiya.
Kamfanonin na cikin gida karkashin kungiyar masu sarrafa magunguna na kungiyar masu masana’antu ta Najeriya.
Hakan na zuwa ne bayan wani baje koli na hadin gwiwa tsakanin gwamnati da masu zaman kansu, tsakanin jihar Kaduna da kungiyar masu hada magunguna a wani taro na shugabannin a Legas.
Taron ya jaddada muhimmancin bangarorin wajen tabbatar da samun kayayyakin kiwon lafiya da suka hada da alluran rigakafi a Najeriya.
Taron ya karbi bakuncin kwamishinonin lafiya, manyan sakatarorin gudanarwa na hukumomin sarrafa magunguna, shugabannin kamfanonin harhada magunguna, masu ruwa da tsaki na kamfanoni da wakilai daga abokan huldar ci gaba.
Cibiyar Bayar da Agajin Gaggawa ta Afirka ta shirya taron don karfafa tsarin samar da kayayyaki da kuma aiwatar da shirin daidaita cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko kan aikin hanyar sadarwa na Kiwon Lafiyar Jama’a Daya.