Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna: Fani-Kayode yayi Zazzafan martani kan bidiyon da ISWAP ta fitar
Tsohon Ministan, Femi Fani-Kayode ya mayar da martani kan faifan bidiyon kungiyar ta’addanci, ISAWP na cin zarafin sauran fasinjojin da aka sace daga jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja.
A ranar 28 ga watan Maris ne wasu ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da fasinjoji sama da 60 daga kan hanyar Abuja zuwa Kaduna.
Tun daga lokacin da aka sace wasu daga cikin wadanda aka sace an sako su, yayin da wasu ke ci gaba da tsare.
Sai dai a cikin faifan bidiyon an ga ‘yan ta’addan na bulala sauran wadanda suka yi garkuwa da su.
Da yake tura bidiyon ‘yan ta’addan a shafinsa na Twitter, tsohon ministan sufurin jiragen sama, Fani-Kayode ya rubuta cewa: “Sauran fasinjojin Abuja zuwa Kaduna da ‘yan ta’addan ISWAP da masu garkuwa da mutane suka yi suna dukansu