Daraktan hukumar horaswa ta kasa, wato NOA, Dolapo Dosunmu ta gargadi ‘yan Nijeriya kan lalata dukiyar al’umma da wuraren kasuwancin da sunan zanga-zangar damuwa da halin da ‘yan Nijeriya ke ciki a kasar Afrika ta Kudu.
Dosunmu ta bayyana hakan ne a ranar Laraba a garin Ibadan dake jihar Oyo a yayin da suke ganawa da manema labarai dangane da zargin kashe ‘yan Nijeriya a kasar Afrika ta Kudu tare da tarwatsa wuraren kasuwancin ‘yan Nijeriya. NOA ta ce akwai bukatar a fahimci cewa kasuwancin da muke ganin kamar mallakin ‘yan Afrika ta Kudu ne, amma ‘yan Nijeriya ke gudanar da shi kuma suke amfana. Sun kara da cewa ‘yan Nijeriya ke aiki a wadannan wuraren, kuma su siyar da abubuwan da ake siyarwa a kamfanukan.
Sannan sun ce wadannan hare-haren na bai wa bata gari dama sace kayayyakin da ake siyarwa a wurin, ta ce; da wannan a karshe ‘yan Nijeriya ne da asara babba.
Dosunmu ta ce abin takaici ne dan Afrika ya rika ganin dan uwansa dan Afrika a matsayin bako. A karshe ta yi kra ga ‘yan Nijeriya da su rungumi zaman lafiya, inda ta ce gwamnatin tarayya tana iya bakin kokarin wajen ganin ‘yan Nijeriya sun samu ‘yanci da zaman lafiya.