Manoman kayan miya a garin Gashuwa, dake Jihar Yobe sun roki Shugaba kasa Muhammadu Buhari ya haramta shigo da tumaturin kasashen waje cikin kasar don taimakawa manoma na gida Nijeriya.
Manoman sun yi wannan kiran ne a zantawar da suka yi da manema labarai da lokuta daban-daban. Wani manomin tumatur, Malam Musa Maitumatur ya ce shigo ta tumaturin kasashen waje ne ke kawo cikas ga ci gaban noman tumatur a gida Nijeriya.
Ya ce, “Matsalar manoman kayan miya ta fara ne daga rashin ingantaccen hanyar da za a adana kayan miyan na tsawon lokaci da wurin ajiya kuma babu wanda ke kokarin tallafawa manoma na gida saboda ana shigo da tumatur daga kasashen waje.”
Wani manomin, Ali Katuzu ya ce manoman na asarar a kalla kashi 50 cikin 100 na abin da suka noma saboda rashin ingantaccen wurin ajiya inda ya kara da cewa tilas ke saka manoman su yanka tumaturin su busar saboda rashin hanyar ajiyar. Ali ya shawarci gwamnati ta kirkiri shiri tsakanin manoma da ‘yan kasuwa ta yadda za a samar da kamfanonin sarrafa tumatur a jihar.
Da ya ke tofa albarkacin bakinsa, wani manomi, Habu Sani ya ce suna noman rani kuma suna iya samar da tumaturin da zai wadatar da yankin Arewa maso Gabas amma kallubalen ajiyar, zirga-zirga da sarrafawa ce suke fama da ita. Ya ce, “Idan ana son kayayyakin cikin gida su inganta, dole sai gwamnati ta haramta shigo da tumaturin kasar waje kamar yadda ta yi a bangaren shinkafa. Manoman Nijeriya ba za su iya bunkasa ba muddin ba a haramta shigo da tumaturin kamfanoni na kasashen waje ba.”