Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya kamata ya rage kudin makaranta a jami’ar sa ta Amurka dake Najeriya, idan har ya rike ilimi da gaske a kasar nan, inji Rabiu Kwankwaso.
Kwankwaso, wanda tsohon gwamnan Kano ne kuma dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar NNPP, ya bayyana a zauren taron na daren yau cewa Abubakar zai tabbatar da cewa ya dauki lamarin Ilimi da muhimmanci idan ya rage kudin makarantar.
KU KARANTA: Yadda Rikicin Kudin Kanana Hukumomi Ta Faro Tsakanin Su Da Gwamnoni – Atiku
Matakin da Abubakar ya dauka na kafa jami’a a matsayin hanyar taimakawa ilimin Najeriya ya yi “kyau”, in ji Mista Kwankwaso a taron da aka nuna a gidan talabijin na Arise TV.
Amma idan aka yi la’akari da yadda karatun zai kasance mai araha, zai taimaka wajen samun damar ilimi, musamman a yankunan arewacin kasar.
Duk da cewa ba a bai wa Atiku Abubakar damar mayar da martani ga kalaman na Mista Kwankwaso ba, sai dai tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce kalaman abokin hamayyar nasa ya saba wa ka’idojin muhawarar, wanda bisa ga dukkan alamu ya jaddada rashin kin yin biyayya a tsakanin su masu muhawara.
Mista Abubakar ya kuma karyata ikirarin da Kwankwaso ya yi cewa PDP ba ta yi wani abin kirki ba a lokacin da ta rike madafun iko na tsawon shekaru 16 daga 1999 zuwa 2015, yana mai jaddada cewa jam’iyyar ta aiwatar da sauye-sauyen da suka mayar da ilimi da tattalin arzikin kasar nan zuwa wani kadami na kaico.
A wani labarin kuma: Yan Sandan Sudan Sun Saki Wani Mai Fafutukar Yaki Da Cin hanci Da Rashawa
An sako wani fitaccen dan siyasar Sudan daga gidan yari kwana guda gabanin kawancen farar hula da ya ke da shi ya rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta farko da sojoji domin kawo karshen takaddamar siyasa da ya haifar da juyin mulkin watan Oktoban 2021.
Dan siyasar Wagdi Salih, wanda aka sake shi ranar Lahadi a ofishin ‘yan sanda a Khartoum babban birnin kasar, yana kan gaba a kwamitin yaki da cin hanci da rashawa da aka kafa bayan hambarar da tsohon shugaban Sudan Omar al-Bashir a shekara ta 2019.