Tsohon mataimakin shugaban nan kuma dan takarar shugabancin kasar nan a inuwar jam’iyyar PDP a zaben 2019, Alhaji Atiku Abubakar, ya yi maraba da gwamna Godwin Obaseki cikin jam’iyyar PDP.
A sakon taya murnar da ya wallafa kan shigar gwamnan PDP, Atiku Abubakar, ya ce “PDP ita ce hakikanin jam’iyyar al’umma”.
“Ka shigo jam’iyyar PDP ne lokacin da aka sauya fasalinta ta yadda take son aiwatar da mulki na gari domin gajiyar ‘yan Najeriya,” in ji tsohon mataimakin shugaban kasar.
https://dimokuradiyya.com.ng/da-dumi-dumi-gwamnan-jihar-godwin-obaseki-ya-koma-jamiyyar-pdp/
Mista Obaseki ya shiga jam’iyyar ne kwana kadan bayan da ya fice daga jam’iyyar APC wacce a cikinta aka zabe shi a karon farko.
A makon da ya wuce ne jam’iyyar APC ta ce Obaseki ba zai iya shiga takara a zaben fitar da gwani ba saboda a cewarta akwai bambamce-bambamce a takardun makarantarsa.