Kwamitin bincike da kwato dukiyar alúmmar Jihar Gombe ya kira tsohon Gwamna Ibrahim Hassan Dankwambo ya yi hanzarin gurfana a gaban Kwamitin tare da ýan gwamnatinsa, domin su yi bayani kan dukiyar alúmma da suka mallakawa kansu.
Shugaban Kwamitin Group Captain Peter Bilal mai ritaya ya bayyanawa Ýan jarida haka jiya a garin Gombe.
”Idan kuwa ba mu sami hadin kansu ba, za mu yi amfani da karfin doka, mu yi musu matsar-gyada domin su dawo da dukiyar alúmma da suka mallakwa kansu ba tare da bin wata kaída ba.