Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a ranar Lahadi, ya yi Allah wadai da kisan wasu makiyaya biyu da wasu ’yan daba suka yi a karamar hukumar Birni Gwari ta jihar.
Jaridar DIMOKURADIYYA ta tuna cewa wasu gungun ‘yan bindiga sun kashe wasu makiyaya biyu da ake zargin ‘yan fashi ne a karamar hukumar Birnin Gwari.
KARANTA WANNAN LABARIN: ‘Yan Najeriya Miliyan 15 Ne Ke Amfana Da Ayyukan Samar Da Ruwan Sha — FG
Bayan haka, Gwamna Nasir El-Rufai, ya gargadi mazauna karamar hukumar da kada su dauki doka a hannunsu ta hanyar lallasa wanda ake zargi.
A wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, kwamishinan ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida ta jihar Kaduna, Mista Samuel Aruwan, ya ce gwamnan, yayin da yake yin Allah wadai da wannan aika-aikar, ya gargadi mazauna yankin da su kasance masu bin doka da oda tare da daina daukar matakin da zai iya haifar da tashin hankali da rushewar doka da oda baki daya.
El-Rufai, yayin da yake nuna matukar damuwarsa game da harin da wasu gungun ‘yan daba suka kai wa makiyaya biyu, ya kuma shawarci mazauna yankin da su daina aika kisan gilla na babu gaira ba sabar.
Ya kuma yi nuni da cewa hanya daya tilo ta bayyana korafe-korafe da abubuwan da suka shafi aikata laifuka ita ce a kai rahoto ga jami’an tsaro domin daukar mataki cikin gaggawa.
Sanarwar ta kuma yi kira ga iyalan wadanda abin ya shafa da su kwantar da hankalinsu tare da umurtar hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike domin kamun kifi da masu aikata laifin.
A wani labarin kuma, 2023: Ban Janye Daga Takarar Shugaban Kasa Ba – Tinubu Ya Magantu
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, ya musanta janyewa daga takarar shugaban Kasa.
Tinubu ya saka wani dan gajeren hoton bidiyonsa a kan wani shafi a yammacin ranar Lahadin nan, a wani yunkuri na karyata jita-jitar da ake yadawa.