Daga Mohammed Gambo Damaturu
Kakakin Majalisar dokokin jihar Yobe Alhaji Ahmed Lawan Mirwa ya kai ziyarar neman ta barruki da kuma murnar samun zama kakakin Majalisar dokokin jiha.
Idan za’a iya tunawa ranar litinin 24 ga watan Yuni na makon nan aka kaddamar da Majalisar dokokin jihar Yobe, wacce itace ta bakwai tun dawowar dimukoradiyya.
Kamar yadda lamarin yake, a yayin da aka samu abun farin ciki, to akan rabashi da ‘yan uwa, abokan arziki da masoya, don haka shima Sabon kakakin Majalisar dokokin jihar Yobe Alhaji Ahmed Lawan Mirwa, ya kai ziyarar neman tabarrukin iyaye da kuma nuna farin cikin samun matsayin kakakin Majalisar dokokin jihar ta Yobe a mahaifar sa da sauran al’uman kewayen Nguru.
Da yake jawabi a fadar Sarkin Nguru, Alhaji Ahmed Lawan Mirwa yace ya taho da sauran abokan sa na Majalisar dokokin jihar Yobe domin neman tabarrikin mai martaba kan sabon matsayin da ya samu.
Mirwa yayiwa Allah godiya da bashi wannan matsayi ya kuma roki al’umar yankin sa da sauran ‘yan jihar Yobe da su taya shi da addu’a domin sauke nauyin da aka daura masa.
A martanin sa, mai martaba Sarkin Nguru Alhaji Mustapha Ibn Kyari ya nuna farin cikin sa kan ziyarar, sannan ya taya kakakin Majalisar murna da wannan karuwa kuma ya bashi tabbacin samun goyon baya shawarwari masu kyau daga masautar.
Sarkin ya kuma ja hankalin Mirwa da ya rungumi kowa domin jihar Yobe ta cigaba.
Tawagar kakakin Majalisar dai ta kunshi Mataimakin sa Alhaji Isah Bello Danchua, mai tsawatarwar Majalisa Alhaji Buba Ibrahim Kalallawa, Membobi mazabun Jajere, Karasuwa, Gulani, Potiskum, Yusufari da dai sauransu.