Muna baƙin cikin sanar da abokan huldarmu na cinikayya cewa rashin wutar lantarki da ake fuskanta a halin yanzu shine na rugujewar layin wutar na Grid a kasa baki daya wanda ya faru da karfe 11:28 na safiya.
Wannan na kunshe ne ta cikin sanarwar da shugaban sashin sadarwa na kamfanin rarraba hasken wutar lantar na Kaduna ya aikowa Dimokuradiyya.
Sanarwar ta ce Don haka muna ba abokan cinikinmu masu girma tabbacin maido da wutar lantarki na yau da kullun da zaran kamdanin dakon wutar lantar na TCN ya dawo mana da kayan aiki.
Muna matukar nadama da rashin jin daɗi sakamakon gazawar tsarin samun wutar lantarkin.
Sa hannu
Abdulazeez Abdullahi
Shugaban, sashin sadarwar na kamfani