Babban Mai binciken kudi na kananan hukumomin jihar Kano Ahmad Tijjani Abdullahi yace sanya hanu akan dokar kula da kashe kudaden kananan hukumomi ta shekara ta 2020 wacce gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje yayi zata taimaka wajen tabbatar da adalci da kuma bin ka’ida yayin kashe kudaden jama’a.
Ahmad Tijjani Abdullahi ya bayyana hakan ne a taron karawa juna sani da aka shiryawa masu binciken kudi na kananan hukumomi 44 dake nan Kano domin sanin dokoki da ka’idojin da ke kunshe a sabuwar dokar a Kaduna.
Bukola Saraki Ya Soki Hukuncin Garƙame Majalisar dokokin jihar Filato
Jihar Kano zata karbi bakuncin gasar matasa ta shekarar 2022
Daga nan sai ya yabawa gwamna Ganduje dangane da yadda ya sanyawa dokar hanu, ya kuma sahale aka gudanar da taron karawa juna sanin domin amfanin ma’aikata.
A jawabinsa yayin taron, shugaban kwamitin kula da dukiyoyin al’umma na majalisar dokokin jihar Kano Salisu Ibrahim Doguwa ya bukaci babbar Mai binciken kudi ta jihar kano Hajiya Amina Inuwa Sa’id da babban Mai binciken kudi na kananan hukumomi da su sake shirya ire-iren wadannan taruka da nufin horar da ma’aikatan su ka’idojin da ke kunshe cikin dokar.
Tunda farko a jawabinsa, kwamishinan kananan hukumomi da Masarautu na jihar Kano Murtala Sule Garo Wanda babban sakataren ma’aikatar Alhaji Ibrahim Ahmad Sagagi ya wakilta ya ce ma’aikatar zata sake shirya makamancin taron da nufin sake horar da masu binciken kudi dabarun gudanar da ayyukan su domin samun sakamako Mai ma’ana.