Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano karkashin jagorancin mai shari’a A.A Liman a ranar Larabar da ta gabata ta yi watsi da karar da hadimin shugaban kasa Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad, ya shigar.
A cikin karar yana kalubalantar nasarar Abdullahi Mahmud Gaya a zaben fidda gwani na jam’iyyar APC na mazabar Gaya/Ajingi/Albasu a ranar 25 ga Mayu, 2022.
A hukuncin da ya yanke, Mai shari’a Liman ya ci gaba da cewa mai shigar da karar ya kasa tabbatar da zargin buga kuri’u da dama, wanda ya hana wakilansa 85 ‘yancin shiga wurin zaben.
KU KARANTA: Na Garzaya Kotu Don Ta Tabbatar Da Gwamnan Legas A Matsayin Mahaifina – Wani Matashi
Hakazalika kotun ta ce wanda ya yi zargin dole ne ya bayar da hujja ba tare da kokwanto ba, yana mai jaddada cewa wanda ya shigar da karar ya gaza sauke nauyin da ke kan kafadarsa a matsayinsa na mai kara.
Idan dai za a iya tunawa Abdullahi Mahmud Gaya ya samu nasara ne da kuri’u 109 a zaben fidda gwani na jam’iyyar APC a kananan hukumomin Gaya/Ajingi/Albasu.
Da yake nuna rashin gamsuwa da sakamakon, Ahmad ya garzaya kotu yana fatan ta soke zaben tare da ba da umarnin sake gudanar da wani sabon zabe da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta gudanar, sai dai a hukuncin da ya yanke mai shari’a Liman ya ce an gudanar da zaben ne daidai da tanade-tanaden zabe, Dokar ta 2022 da aka yiwa kwaskwarima.
Barista Abubakar Muhammad daga Nuraini Jimoh Law Firm ya godewa kotun da ta yanke hukuncin da ya dace.
A nasa bangaren, lauyan Bashir Ahmad, Barista Lawan Idris ya ce za su gwada hukuncin a kotun daukaka kara.
Bayan da kotun ta yanke hukuncin, dan majalisar mai ci a mazabar ya ce hukuncin da ya bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwani kuma dan takarar majalisar wakilai ta Gaya, Ajingi, karamar hukumar Albasu ta jihar Kano ga jam’iyyar nasara ce ta adalci.
Hakazalika, a wata sanarwar manema labarai, wanda babban hadiminsa na majalisar, Ibrahim Umar ya raba wa manema labarai, ya ce “Ina maraba da hukuncin da alkalin babbar kotun tarayya, Kano ya yanke, nasara ce ta tabbatar da adalci.
Hon. Abdullahi Mahmud Gaya ya kuma mika godiyarsa ga daukacin magoya bayansa bisa ga addu’o’in da suke yi da kuma goyon bayan da suka ba shi, yana mai cewa, zai ci gaba da yin aiki tukuru wajen ganin an samar da ci gaba da bunkasar rayuwar bil’adama da samar da ababen more rayuwa da aka samu a lungu da sako na mazabar, ya kara da cewa a matsayina na mai hidima na taba rayuwa a mazabana ta hanya mai inganci.