Hukumar kula da zirga zirga-zirgar ababan hawa ta jihar Kano KAROTA ta sanar da korar wani jami’in ta RTA II Jamilu Gambo, bayan wuce gona da iri wajen zartar da hukunci.
Mai magana da yawun hukumar Nabulisi Abubakar cikin wata sanarwa da ya aikowa da jaridar Dimokuraɗiyya a yau Alhamis, ya bayyana cewa sun zartar da wannan hukuncin ne bayan da jami’in ya yankawa wani mai motar Tirela Tayar Mota, bayan da mai motar ya aikata wani laifi na daban, wanda hakan ya sanya suka yi hatsaniya da direban motar.
Lamarin dai ya faru ne a yammacin Jiya, Laraba akan hanyar Kano zuwa Hadeja, wanda kuma sakamakon hakan ya haddasa cinkoson ababan hawa a yankin kan titin.
Hakan ta sanya a yau, aka shiga taron gaggawa kan batun tsakanin hukumar da kuma rundunar yan sanda ta jihar, kuma sun fahimci cewa abinda jami’in Karotan ya aikata baya daga cikin ka’idar aiki, hakan ya sanya suka yanke hukuncin korar sa.
Shugaban Hukumar KAROTA Hon. Baffa Babba Ɗan’agundi ya godewa shugabancin kungiyar NARTO reshen jihar Kano, bisa yadda suka shiga tsakani a jiyan tare da samar da masalaha.