Rahotanni daga karamar hukumar Takai a jihar Kano na cewa a daren jiya yan bindiga sun shiga garin ƙarfi dake dake yankin Takai ɗin, inda suka kashe mutane 6, suka raunata 2 sannan suka tafi da Sarkin garin wato Dagacin AbdulHayatu Karfi.
Wani mazaunin garin a zantawar Dimokuraɗiyya da shi ya bayyana cewa yan bindigar sun shiga garin ne da karfe 12 saura na dare suna harbe-harbe da bindiga.
”Wajen 12 shaura na dare yan bindiga sun shigo Karfi dake Takai suna harbe-harbe, mutane ma sun dauka masu babura ne suke wasa, sai ganin su akai akan babura sun zo gidan Sarkin Ƙarfi suka dauke shi suka tafi dashi”
Ya sheda mana cewa yan bindigar sun shigo ne daga bangaren kudancin garin inda sukai iyaka da jihar Bauchi, sun harbi mutane 8 a hanyar komawar su bayan sun yi garkuwa da Sarkin.
Shida daga cikin wadanda aka harba sun riga mu gidan gaskiya, yayin da ragowar mutum 2 suke kwance asibiti.
A halin yanzu ana shirye-shiryen yin Jana’izar wadanda suka rasu a garin na karfi.
Dimokuraɗiyya ta tuntubi mai magana da yawun Rundunar Yan sandan Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa, inda kuma ya shida mana cewa har kawo yanzu ya Gaza samun DPO din Takai Ballantana ya samu karin bayani.
Kiyawa yayi alƙawarin karin haske bayan ya same shi.