Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya ce shi ba zai tilastawa Amurkawa sanya takunkumin fuska ba saboda annobar cutar korona.
A baya-bayan nan ne dai aka ga Trump ya sanya takunkumi a karon farko bayan matsin lambar da ya sha daga ‘yan adawa tun bayan bullar annobar cutar korona a kasar ta Amurka.
Trump ya jaddada cewa; kamata ya yi a bar kowanne dan kasa ya wataya kamar yadda dokar kasa ta bashi dama. Trump ya tabbatar da hakan ne a yayin wata hira da kafar talabijin ta Fox a ranar Jumma’a,
Trump ya maida bayani ne kwana guda da Babban likitan da ke jagorantar yaki da cutar a Amurka Dr Anthony Fauchi, ya yi kira ga yan siyasa da jagorori su ci gaba da kira ga mabiyansu, su rika sanya takunkumi.