Daga: Abbas Yakubu Yaura
Sarkin Kano na 14, Muhammad Sanusi, ya bayyana sayen kuri’u a matsayin mugun karfi da ke barazana ga tsarkin tsarin dimokradiyya a Najeriya.
Sanusi ya yi wannan maganar ne a yayin taron shekara hudu na Penpushing Media, mai taken: (“Dokar kafafen yada labarai na zamani: rashin tsaro da kuma Elections Accountability in Nigeria) ”, wanda aka gudanar a dakin karatu na Olusegun Obasanjo (OOPL) da ke Abeokuta, jihar Ogun.
KARANTA WANNAN LABARIN: https://dimokuradiyya.com.ng/mai-bada-maganin-gargajiya-yayi-wa-yar-shekara-14-fyade-a-adamawa/
Ya ce sayen kuri’u ya saba wa ka’idojin dimokuradiyya da kuma rashin mutunta dokar zabe, da kuma tsarkin zaben.
Sanusi musamman ya nuna damuwarsa kan yadda masu kada kuri’a ke nuna katin zabe da aka buga da babban yatsa a matsayin shaida na cinikin kuri’unsu ga ‘yan siyasa.
Ya ce, “Don haka kamar yadda ‘yan Nijeriya ke yaba wa ‘yan siyasa don inganta doka, muna bukatar mu yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi taka-tsan-tsan, su kuma cibiyoyi da su mutunta ayyukansu tare da kasancewa masu tsaka-tsaki da kuma tabbatar da adalci da gaskiya.
“Daya daga cikin manyan hanyoyin da ake bi wajen murguda zabe a sabuwar dokar ita ce manufar sayen kuri’u, kuma wannan rashin mutunta dokar zabe a asirce ne.
“Dole ne al’ummar Najeriya da ‘yan kasar su hada kai don tabbatar da tsarkin katin zabe da kuma sirrin zabensu.”
“Muna bukatar mu tabbatar da cewa wadanda muka zaba a mukaman su ne wadanda aka sanar.”