Kasashe kusan 50 ne za su halarci wani taraon gaggawa karkashin shirin Majalisar Dinkin Duniya kan halin da ake ciki a Sudan tun bayan da sojoji suka hambarar da gwamnatin Abdallah Hamdok.
Rikicin da ake samu a kasar Sudan tun bayan juyin mulkin da ya juye zuwa tarzoma ya janyo hankalin duniya musamman yadda sojoji suka fara amfani da karfin tuwo wajen fara harbin kan mai uwa da wabi da kuma tarwatsa masu zanga-zangar.
A wata wasika da kasashen 48 suka aike wa Majalisar Dinkin Duniyar mai dauke da sa hannun jakadan Burtaniya Simon Manley ta jadadda bukatar da ke akwai na tattaunawa tsakanin kasashe don magance matsalar da ta kunno a Sudan din.
A halin da ake ciki dai bayanai sun ce, dubban mutanen ne suka tsere daga Sudan din sakamakon tsoron abinda kaje ya zo, tun bayan rikicin da ya ki ci yaki cinyewa saboda juyin mulkin karkashin jagorancin Abdel Fattah Al-Burhan.
Ya zuwa yanzu sojoji sun hallaka mutane kusan 15 tare da jikkata 170 sai dai tuni ‘yan sanda suka musanta kisan.
Wannan dauki ba dadin da ke faruwa a kasar ne ya tilasta wa kasashen shirya taron karkashin jagorancin Majalisar Dinkin Duniya don shawo kan matsalar kafin ta kai ga karasa rushe kasar dungurungun.