Malamin Addinin Musuluncin nan A Najeriya Sheik Ahmad Gumi ya ce a lokacin da Annabi (Sallallahu alaihi Wasallama) yake a raye da dama cikin kafirai sun yi masa abinda bai dace ba.
Amma duk cikin kafirai da suka yi masa wani abu da nufin Tozarta shi, ba wanda aka taba hantara ko a kashe shi.
Yayi wannan martani ne yayin da yake karatu a Masallacin Juma’arsa na Kaduna, wanda yake magana kan kisan wata Daliba Kirista a jihar Sokoto, bayan da tayi kalaman batanci ga Shugaban Halitta SAW.
Ya kuma ce Babbar Hanyar da Musulmai zasu nuna suna son Annabi Sallallahu alaihi Wasallama, shine biyayya ga fadinsa, da kuma irin yadda yake addini, maimakon kashe mutane da kuma tayar da zaune tsaye.
Ya ce babban abun ci gaba ne yadda Musulmi da Kiristoci suka yadda domin zama tare a Najeriya, a ganinsa kamata yayi a taimaki zaman lafiyar ta hanyar bin doka da oda, kan duk wani abu daya taso a tsakanin bangarorin biyu.