KASU ta yi Allah wadai da kalaman Shugaban ASUU akan Jami’o’in Jihohi
Hukumar gudanarwar Jami’ar Jihar Kaduna, a ranar Asabar ɗin nan, ta caccaki Shugaban Kungiyar Malaman Jami’o’i ta kasa, ASUU, Farfesa Victor Emmanuel Osodeke, kan kalaman da ya yi na cewa wasu jami’o’in mallakar Jihohi a Najeriya basu cancanta ba, kuma basa bada ingantaccen ilmi.
Shugaban ASUU, a lokacin da yake tattaunawa kai tsaye kan wasu al’amura na Ƙungiyar, ya bayyana wasu jami’o’in mallakar Jihohi a Najeriya a matsayin bara-gurbi.
KARANTA WANNAN LABARIN: Sai Na Kawo Karshen Fasa Bututun Mai A Najeriya–Kwamandan Hukumar NSCDC
Da yake mayar da martani a cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na Jami’ar Jihar Kaduna (PRO), Adamu Nuhu Bargo ya fitar a madadin hukumar, ya ce
Duniya ta cika da mamaki da kalaman yaudara da batanci da Shugaban ASUU na kasa ya yi.
A cewar sanarwar, ta bayyana a fili cewa, da irin wannan furuci, ASUU ba ta fafutukar ganin an inganta tsarin ilimi a Najeriya ba, sai dai kawai don raɗin kansu tare da abinda zasu samu.
Sanarwar ta yi mamakin ko Farfesan Kimiyyar Ƙasa ya fahimci ainihin abin da kalmar “quack” ke wakilta.
” Kalmar Quack yana nufin mutumin da rashin gaskiya ya yi ikirarin cewa yana da ilimi da fasaha a wani fanni wanda ba shi da tushe, kamar yadda kwararru suka yi misali,” in ji shi.
Ya ce, KASU sabuwar jami’a ce kuma jami’a ta biyu da ake nema a jihar, haka kuma ita ce jami’ar da ta fi kowacce girma a Nijeriya, wadda aka kafa shekaru 18 da suka gabata tare da manyan malamai kamar su Farfesa Idris A. Abdulkadir da OFR da Farfesa Abubakar. A. Rasheed, MFR, a Matsayin kwamitin gudanarwa, ya kara da cewa malaman sun tabbatar da cewa ba a taba yin kasa a gwiwa ba wajen nada kwararrun malamai.
A Wani Labarin kuma: Maikyau Ya Sha Rantsuwar Kama Aiki, A Matsayin Sabon Shugaban NBA