Ya zuwa yanzu a bayanin da NCDC suka wallafa a shafinsu na Twitter sun tabbatar da cewa; mutum 1,472 ne suka warke daga cutar Korona a Nijeriya a yayin da 176 suka mutu inda kuma 5, 621 suka kamu da cutar jimilla baki daya.
NCDC sun ce a jiya kawai an samu mutum 176 da ba suke dauke da cutar, wanda suka fito daga jihohi sha uku na Nijeriya wanda ya hada da; 95 a Legas, 31 a Oyo, sai kuma Abuja, inda aka samu karin mutane 11.
Sauran jihohin sun hada da Borno da Neja masu karin mutane 8-8, sai Jigawa mutane 6, a Kaduna kuma mutane 4. Jihar Anambra ke biye bayan samun karin 3, sai jihohin Nasarawa, Ribas, da Bauchi, yayin da Zamfara da Binuwe ke da mutum guda-guda.
Jihar Legas ke sahun gaba wajen yawan mutanen da suka harbu da cutar a jumlace, inda take da 2,373, sai Kano mai 761, sai Abuja mai mutane 397, Katsina na da 239, Borno da Bauchi na da 212 kowacce, sai Jigawa mai 197.