-Gwamnonin PDP Sun Goyi Baya.
A yayin taron Kasa kan batun tsaro da aka yi a Abuja, a tsakanin Shugaban kasa, gwamnoni da sauran masu ruwa da taski, Kungiyar Gwamnonin PDP na jihohin Najeriya sun Aminta da a bawa jihohi dama su kirkiro Rundunar ‘Yansandan Jihohi.
Shi kuwa Gwamnan Jihar Ekiti Kayode Fayemi, ya ce Kungiyar Gwamnoni a dunkule ba su dauki matsaya ba.
Kungiyar Gwamnonin na PDP, sun ce sun lura ana kokarin siyasantar da al’amarin tsaro ne kawai.