By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnan jihar Akwa Ibom, Mista Udom Emmanuel, ya yi kira ga ‘yan kasa dasu yi watsi da duk wani dan siyasa dake shirin tayar da hankali da kuma kawo cikas ga zaman lafiya a jihar.
Da yake magana a ranar Asabar a Uyo yayin wani watsa shirye-shiryen Kirsimeti ga al’ummar jihar, Emmanuel yace zaman lafiyar da aka samu a jihar ne ya haifar da kirkire-kirkire da ruhin kasuwanci da aka shaida a ‘yan kwanakin nan.
Ya yi kira ga ‘yan siyasa dasu nisanci daci su rungumi ‘yan uwantaka maimakon haka.
“Mutanenmu sun sami kwanciyar hankali a tsakaninsu. Zaman lafiya yasa mun shiga cikin rijiyoyin kirkire-kirkire da al’adun kasuwanci na jama’armu, musamman matasa. Dole ne mu kiyaye wannan zaman lafiya da kowane zaren halittunmu
“Kuma bari in kara da cewa, duk wanda ke da burin samun mulki ta hanyar cin zarafi ga jama’arsa, zai yi mulki da tashin hankali. Allah ya sa lokacin zaman lafiya da Kirsimeti ke wakilta, kada mu sake ganin Jiharmu ta shiga cikin irin wannan tashe-tashen hankula masu nasaba da siyasa,” inji shi.