Ko kaɗan ba mu damu ba – PDP ta caccaki APC kan ƙalubalantar zaɓen Gwamnan Osun
Jam’iyyar PDP reshen jihar Osun ta mayar da martani kan matakin da jam’iyyar APC da Gwamna Gboyega Oyetola suka ɗauka na ƙalubalantar sakamakon zaɓen Gwamnan da aka gudanar a ranar 16 ga watan Yuli a gaban Kotun sauraron Ƙararrakin Zaɓe.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ya kamata tun farko masu adawa da Tinubu su taimaki Kirista ya samu tikitin APC – Oshiomhole
Jam’iyyar PDP ta ce har yanzu ba a mika mata wata takardar neman zabe ba, inda ta ƙara da cewa zaɓaɓɓen Gwamna ko jam’iyyar ba su damu da ƙarar da ake zargin ta kai mata ba.
Shugaban jam’iyyar APC na jihar Osun, Gboyega Famoodun, a ranar Alhamis, ya bayyana cewa jam’iyyar ta kammala shirye-shiryen gurfanar da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), PDP da kuma zababben Gwamnan Jihar, Sanata Ademola Adeleke a gaban Kotun sauraren Ƙararrakin Zaɓe kan sakamakon zaɓen.
Da take mayar da martani, PDP ta bayyana matakin a matsayin “tafiya maras amfani da aikin banza”, ta kuma yi Allah-wadai da matakin, tare da ayyana shi a matsayin “masu adawa da mutane kuma ƙalubale ne na nufin Allah”.
A wata sanarwa da Shugaban Kwamitin riko na jam’iyyar PDP, Dr Akindele Adekunle ya fitar, ya bayyana cewa wa’adin da mutanen Osun suka ba Adeleke ya zo.
Ya kara da cewa, “Har yanzu ba a kai mana ko wane irin korafin zabe ba. Jam’iyya ko Gwamna mai jiran gado ba su damu da korafin da ake zargin cewa zaben da ya haifar da wanda ya lashe zaben ya kasance na bin tsarin dimokaradiyya a duniya.
“Wannan zaben da aka kammala ya wuce gwajin mafi kyawu a cikin tsarin zabe tare da aiwatar da ingantaccen tsarin zaben wanda ya rufe duk wani makirci na jam’iyyar All Progressives Congress (APC).”