Tun bayan kawo sabon mai horas da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Juventus kuma tsohon ɗan wasansu wato Andre Pirlo ya bayyana cewar zai sallami wasu ‘yan wasan domin samo wasu sababbin jini dazasu maye gurbinsu.
Hakan kuwa a kayi daga zuwansa ya ambata cewar bazai tafi da wasu ‘yan wasan ba inda wasu daga cikinsu har sunansu ya ambata ƙarara, amma ganin kan cewa shi kansa Pirlo sabon jini ne a fannin horas wa ana zaton zai kawo sababbin jini masu
ƙananan shekaru ashe abin ba haka bane.
Inda masu iya magana na cewa ana zaton wuta a maƙera sai aka sameta a masaƙa inda akaga Juventus na sayen masu shekaru sama da 30, ko a jiya ta sayi manyan ‘yan wasa guda biyu daga manyan ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa a nahiyar turai.
A daren jiya dai Juventus ta ɗauki Louis Suarez daga Barcelona da kuma Eden Dzeko daga ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta A.S Roma dake ƙasar ta Italiya inda dukkaninsu tsofafin ‘yan wasa ne.
Burin ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Juventus shine ta lashe gasar zakarun nahiyar turai inda sabo da haka suka sayi shahararren ɗan wasa Christiano Ronaldo daga Real Madrid tun a shekaru biyu da suka gabata.
Abin tambayar anan shine shin tsofaffin ‘yan wasan ƙungiyar ƙwallon ƙafan da Juventus take tarawa zasu fitar dasu daga gaci na cimma burin ƙungiyar wajen lashe gasar zakarun nahiyar turai? tambayar da www.dimokuradiyya.com.ng ta yiwa Jameela mai goyon bayan ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Juventus wadda tabi Christiano Ronaldo can wanda daman can shi take goyon baya tun lokacin yana Madrid.
“Ina ganin sayen manyan ‘yanwasa masu shekaru ba shine zaisa Juventus ta lashe gasar zakarun nahiyar turai ba, dole sai sun sayi ‘yan wasa masu ƙananun shekaru, tunda daga shekarar 2000 zuwa 2017 Juventus tazo wasan ƙarshe na gasar zakarun turai har sau 3 amma basuyi nasara awasa ko guda ba, ni inson Ronaldo ya lashe gasar zakarun turai a Juventus kamar yadda ya lashe a Manchester United da kuma Real Madrid”