Kotun Bangladesh ta yanke wa mutane 16 hukuncin kisa saboda samun su da laifin kashe wata daliba ta hanyar cinna mata wuta bayan sun zarge ta da yi wa Malaminta karyar cin zarafinta.
A cikin watan Afrilun da ya gabata ne, Nusrat Jahan Rafi mai shekara 19 ta gamu da ajalinta a wani karamin gari da ake kira Feni wanda ke da tazarar kilmita 160 daga babban birnin Dhaka.
Malamin da Nusrat ta zarga da kokarin lalata da ita, da wasu mata biyu abokan karatunta, na ckin wadanda kotun ta yanke wa hukuncin kisa.
Kisan matashiyar ya tayar da hankulan jama’ar Bangladesh, yayin da aka gudanar da jerin zanga-zangar neman yi bi mata kadi.
Shari’ar da kotun ta na cikin shari’o’i mafi daukar hankali da aka gudanar cikin gaggawa a kasar wadda ke shafe tsawon shekaru kafin kammala sauraren bahasi kan zarge-zargen lalata da mata. Kodayake lauyoyin mutanen da aka daure sun ce, za su daukaka kara domin kalubalantar hukuncin kisa akansu.