Ƙasar Koriya ta hannun hukumar agajin ta mai suna (KOICA) ta bai wa ma’aikatan Najeriya kyautar takunkumin hanci domin hana yaɗuwar cutar Korona.
Shugaban makarantar ma’aikatan Najeriya, Abdul-Ganiyu Obatoyinbo ya karɓi kayan da aka kawo, kamar yadda yake ƙunshe cikin takardar da hukumar ta fitar ranar Laraba.
Da yake jawabi a wajen taron, shugaban KOICA na Najeria Mista Woochan Chang, ya ce sun yi hakan ne domin taimaka wa yaƙi da cutar da kuma taimaka wa abokan hulɗarsu a lokacin tsananin da ake ciki.
https://dimokuradiyya.com.ng/korona-nijeriya-za-ta-amfana-da-naira-biliyan-43-daga-bankin-duniya/
Mista Woochan ya ce, agajin ya zo a lokacin da ya dace domin taimakawa a ranar takunkumi ta duniya da kuma gangamin #MaskOnNaija na ba wa mutane ƙwarin gwiwar yin amfani da takunkumin don kariya daga cutar ta Korona.
Shugaban makarantar ya gode wa hukumar, tare da cewa takunkumin zai taimaka sosai wajen hana yaduwar annobar.