Gwamnatin Kano ta ce almajirai 193 ne suka kamu da cutar coronavirus a jihar, lamarin da ya haifar da damuwa game da mayar da almajirai jihohinsu.
Da yake bayani game da rufe makarantun Allo a faɗin jihar, Kwamishinan ilimi Sunusi Muhammad Kiru, ya ce an kwashe aƙalla almajirai 1,500 daga jihar Kano zuwa jihohinsu, ita kuma aka dawo mata da guda 400.
Kwamishinan ya ce, “Lokaci ya wuce na alarammomi su riƙa kwaso almajirai da ba su ma san inda almajiran suke kwana ba”, don haka wajibi ne duk mai son buɗe makarantar allo a jihar ya samar da ɗakunan kwanan almajirai.
https://dimokuradiyya.com.ng/gwamnatin-kano-ta-maishe-da-almajirai-400-jihar-katsina/
Hakan na zuwa ne lokacin da gwamnan Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya cire dokar kulle a fadin jihar face daga 10.00 na dare zuwa 4.00 na asuba.
Da yake jawabi, shugaban kwamitin yaki da cutar Korona a Kano, Dakta Tijjani Hussain, ya ce mutum ɗaya ne aka samu yana ɗauke da ƙwayar cutar daga cikin mutum 2,000 da aka yi wa gwaji na gida-gida a ƙaramar Hukumar Nassarwa.
A cewarsa hakan ya saɓa da rahoton hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa (NCDC) da ya ambato ƙaramar hukumar cikin jerin wanda suka fi samun masu ɗauke da cutar.