Ƙungiyar Raya Tattalin Arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS), ta ba da tallafin hatsi tan 3,999 ga masu ƙaramin ƙarfi a Najeriya.
Kwamishinan ECOWAS Mista Sékou Sangaré ya bayyana hakan lokacin da ya miƙa kayan ga Ministar Agaji da Walwalar Al’umma, Sa’adiya Umar Faruq.
Ya ce kyautar hatsin da suka bayar ƙari ne a taimakawan da ƙungiyar ta bayar a Najeriya daga lokacin ɓullar annobar Korona tun a ranar 27 ga watan Fabrairun 2020, zuwa yanzu.
Sangaré ya ce, ƙungiyar ta ba da tallafin ne bayan tantance wuraren da ke da matsala da matuƙar buƙatar, inda suka gano fiye da mutum miliyan 7,087,102 da suke fama da yunwa a Najeriya, musamman waɗanda ke sansanin gudun hijira da yara masu tasowa.
Ya kuma ce akwai wasu ƙungiyoyin agaji da suka yi haɗaka da su wajen kawo tallafin a Najeriya da sauran ƙasashen Afirka.
A bayaninta na godiya, Ministar ta yi godiya da tallafin da ECOWAS ɗin ta kawo, inda ta ce taimakon ya zo a lokacin da zai yi wa waɗanda annobar Korona ta shafi tattalin arzikinsu amfani.