Gwamnatin Tarayya ta ba da izinin yin tafiye-tafiye tsakanin dukkan jihohin Najeriya daga ranar 1 ga watan Yulin da zamu shiga.
Hakan na zuwa ne a ranar Litinin da Shugaba Muhammadu Buhari ya karbi rahoto na biyar daga kwamitinsa na kar-ta-kwana kan yaki da cutar coronavirus, kan halin da ake ciki game da cutar a kasar.
“Ina farin cikin shaida muku cewa Shugaban Kasa… ya amince, sai dai ‘yan sauye-sauyen da za a sanar a nan gaba”. inji Bos Mustapha, shugaban kwamitin.
Sai dai ya ce tafiye-tafiyen za su fara ne daga ranar 1 ga watan Yuli, tsakanin karfe 5 na Asuba zuwa 10 na dare da a baya aka kebance manyan motoci masu dakon kayan abinci da kayan gwari da shi.