Gwamnatin tarayya ta sanya jirgin Emirate cikin jerin waɗanda ta haramtawa shigowa Najeriya daga ranar Litinin, 21 ga watan Satumba, 2020.
Ministan sufurin jiragen sama, Sanata Hadi Sirika ne ya wallafa hakan a shafinsa na twitter.
Gabanin buɗe zirga-zirgar jiragen ƙasashen waje a ranar 5 ga watan Satumba, cewar gwamnatin tarayya ta hana jiragen ƙasa 10 shigowa ƙasar nan.
Daga cikin jiragen akwai Lufthansa, da Air France da Etihad da KLM da Air Namibia, da dai sauransu.
Haka nan kuma a daidai wannan lokacin suka bar wasu jiragen da suka haɗa da Emirates da Egypt Air da British Airways da Ethiopia da AWA, da sauransu su ci gaba da shigowa.
Sai dai kuma a daren jiya Ministan ya bayyana cewar an haramtawa jirgin Emirates shigowa, wanda hakan ya sa ya fita daga jerin jiragen da aka aminta su shigo can baya.
Sirika ya ce matakin ya biyo bayan taron da suka yi ne da ƙaramin kwamitin shugaban ƙasa na yaƙi da annobar Korona da Jakadan Kungiyar Tarayyar Turai (EU).
Ambasada Ketil Karlsen, wanda shi ne babban jami’in EU a Najeriya da ECOWAS, ya jagoranci jakadun ƙasashen turan zuwa taron da aka gudanar.
Maƙasudin taron shi ne, gwamnatin tarayya ta ƙara yin duba da matakin da ta ɗauka na hana shigowar jiragen daga ƙasashen Turai.
Sirika ya bayyana cewar an samu ci gaba a taron, sai dai an ƙara Emirates cikin sahun jiragen da aka hana shigowa Najeriya.
“Kwamitin da shugaban ƙasa ya naɗa ya yi taro da jakadun ƙasashe ’yan ƙungiyar tarayyar Turai (EU), domin tattaunawa kan hana shigowar jiragen irin su Lufthansa da Air France/KLM.”
“Emirates kuma an saka su cikin jerin waɗanda aka haramtawa shigowa, daga ranar Litinin, 21 ga watan satumba, 2020.”
Ana kyautata zaton gwamnatin tarayya ta ɗauki matakin ne sakamakon hana bayar da biza ta shiga hadaddiyar daular larabawa (UAE) da gwamnatin su ta yi.
Najeriya ta sha alwashin hana jiragen ƙasashen da ba su yarda a shiga ƙasashensu ba shigowa ƙasarta.