‘Yan Najeriya 327 da suka maƙale sakamakon dokar kulle a Birtaniya sun baro birnin Landan zuwa gida zuwa gida Najeriya.
Jami’ar hulɗa da Jama’a ta Ministan Harkoin Wajen, Sarah Sanda ta ce mutanen da suka taso daga filin jirgi na Gatwick, London, za su sauka ne a Abuja.
Sarah Sanda ta ce “sun baro London da misalin 11.15 na safiyar Lahadi 9 ga Agusta, a cikin jirgin kamfanin Air Peace”.
https://dimokuradiyya.com.ng/korona-najeriya-ta-kwaso-mutane-317-daga-birtaniya/
Tun bayan sassauta kullen COVID-19 Gwamnatin Tarayya ke ta kwaso ’yan Najeriya da suka maƙale a wasu ƙasashe zuwa gida.
Ko a ranar Asabar gwamnati ta kwaso wasu mutum 323 daga Birtaniyan wadanda ta sauke su a Legas.
Akan tantance dukkannin wadanda aka kwaso ɗin sannan a killace su na tsawonmtsawon biyu domin tabbatar da ba su harbu da cutar Korona ba kafin su koma ga iyalansu.