Otel-Otel dake karamar hukumar Karu na jihar Nasarawa sun koka kan rashin samun kasuwa sakamakon annobar cutar korona da ya addabi kasarnan.
Wasu ma’aikatan otal din da suka yi hira da manema labarai sun ce sun tafka asara sakamakon dokar hana fita da gwamnati ta sanya saboda kare yaduwar cutar korona.
Rita Uche, wata ma’aikaciyar otal din Rovac Guest Inn, ta ce yanzu kwastomomi basa zuwa, inda ya ce kasuwancinsu ya samu matsala sakamakon annobar.
Ta ce kafin annobar, suna samun kasuwa sosai, amma a cikin watanni uku da suka wuce, musamman lokacin dokar hana fita, ko naira 500 ba a samu a otal dinsu.
Ta alakanta rashin zuwan kwastomomi da tsoron kamuwa da cutar korona, saboda yanzu jama’a da dama da tsoron amfani da kayan da kowa ke iya amfani da shi.