Gwamnatin Chadi ta ce daga Juma’a mai zuwa babu shiga da fita a birnin N’Djamena a wani yunkurin da gwamnatin ke yi na dakile cutar korona wacce ke ci gaba da yaduwa a kasar.
Sanarwar da gwamnati ta fitar ta ce mutum 117 da suka kamu da cutar a Chadi, to mutum 115 sun fito ne daga N’Djamena wanda hakan ya zame musu dole su dauki matakin kariya, saboda haka motocin daukar abinci kawai da na kayayyaki za a baiwa izinin shiga da fita birnin.
Ya zuwa yanzu mutum 10 suka mutu sakamakon wannan annoba a kasar.