Daga: Abbas Yakubu Yaura
A ranar Alhamis ne wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta tsayar da ranar 12 ga watan Oktoba domin cigaba da sauraren karar da ke neman haramtawa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu takara a zaben 2023 bisa zarginsa da yin shedar takardun bogi.
Mai shari’a Obiora Egwuatu ya sanya sabuwar ranar ne domin baiwa masu shigar da kara damar kammala gabatar da shirye-shiryensu da musaya kamar yadda doka ta tanada kafin ranar da aka tsayar.
KARANTA WANNAN LABARIN: An Tsare Wani Jirgin Ruwa Da Ake Zargin Na Ɓarayin Danyen Mai Ne
Tinubu, wanda shi ne babban wanda ake tuhuma a cikin takardar shedar bogi, duk da haka, ya yi aiki da wani babban Lauyan Najeriya, Mista Babatunde Ogala, don ba shi damar kare kansa.
A zaman na ranar Alhamis, Lauyan jam’iyyar Action Alliance wanda ya shigar da karar, Mista Ukpai Ukairo, ya shaida wa kotun cewa ya samu sanarwar kin amincewa da matakin farko daga Tinubu yana rokon kotun da kada ta yi la’akari da karar da ake yi masa bisa wasu dalilai.
Daga cikin dalilan, Tinubu ya yi ikirarin cewa hasashen takardar shedar bogi da aka yi masa ya samo asali ne daga fom din zaben shekarar 1999 da ya mika wa hukumar zabe ta lokacin.
Ya kuma yi ikirarin cewa rahoton majalisar dokokin jihar Legas da ta yi masa bincike a kan zargin takardar shaidar jabu shi ne babban ginshikin sabuwar karar, don haka ya zama haramun.
Sai dai Ukairo ya shaida wa kotun cewa za a magance ikirari da tsohon gwamnan jihar Legas ya yi musamman kan dokar da ta haramta a shari’ar da za ta biyo baya.
Ukairo ya shaidawa Alkalin cewa ikirarin da Tinubu ya yi ta bakin lauyan sa dole ne a yi shi a hukumance kuma a yi masa aiki don ba shi damar amsa yadda ya kamata.
Yayin da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) wadda ita ce ta 1 da ake kara a shari’ar, ta nemi lokaci domin ta mayar da martani kan karar, jam’iyyar APC ba ta samu wakilci a kotu ba duk da hujjojin shigar da kara a kanta.
A kan haka ne alkalin ya dage sauraron karar har zuwa ranar 12 ga watan Oktoba, domin bangarorin su sanya gidajensu domin sauraron karar da ake zarginsu da takardar shaidar jabu.
Bugu da kari Egwuatu ya umarci mai karar da ya shirya tsaf domin gabatar da shaidunsa a ranar da aka dage sauraron karar domin ya tabbatar da karar sa akan Tinubu.
A ranar 21 ga watan Yuni ne jam’iyyar Action Alliance ta bukaci wata babbar kotun tarayya da ta hana hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa shigar da sunan jam’iyyar APC a cikin zaben shugaban kasa na 2023.
Mai shigar da karar a cikin takardar sammacin mai lamba: FHC/ABJ/CS/954/2022, ya fayyace bukatarsa ne kan ikirarin cewa jam’iyyar APC da dan takararta na shugaban kasa, Bola Tinubu ba su cancanci shiga zaben shugaban kasa na 2023 ba bisa zargin Tinubu da yin jabun takardu a shekarar 1999.