• Kutu ta bada belin din jarumin wasan kwai-kwaiyon ne bayan zamar da ta yi a yau Alhamis.
• Wanda ake zargin zai biya naira milliyan biyu kafin a sake shi.
• “Dokar kasa ce ta bada damar asakeshi ba son Rai ba” inji Mai shari’ar Kotun.
Babban Kotun jihar Legas da ke zaman ta a Ikeja, ta bada belin Olanrewaju Omiyinka, wanda aka fi sanida, Baba Ijesha, a kan kudi Naira milliyan biyu, bisa zargin sa da hannu a yin fyade, da kuma cin zarafin kananan Yara.
Mai shari’a oluwatoyin Taiwo ce, ta bada belin dan wasan kwai-kwaiyon a yau Alhamis, a matsayin daya daga cikin yancin da ya ke dashi.
KARANTA WANNAN LABARIN:An yi karkuwa da mutun 12 a jihar Kaduna
A cewar Mai shari’ar “Belin da ta bai wa wanda ake zargin, dama ce da dokar kasa ta bashi, ba na son Rai ba. Inda ta ce, belin din, zai bada damar sakin shi ne daga tsare shi da a kayi, amma zai dunga zuwa Kotun, a duk lokacin da bukatar hakan ta taso” inji ta.
Ta kuma ce, “sakin na shi na dan wani lokaci ne ta-kaitacce, da bazai wuce lokacin da ake sauraran karar ba. Inda ta kuma ce, kudin belin din ya kai Naira milliyan biyu, Inda kuma wanda ake zargin, zai kawo manyan mutane biyu, dasu kafi karfin kudin.” Inji ta.
Comments 1