By Abbas Yakubu Yaura
Kotun hukunta laifuka ta musamman da ke Ikeja karkashin jagorancin mai shari’a Mojisola Dada ta bayar da belin fitaccen jarumin shafin Instagram, Ismaila Mustapha, wanda aka fi sani da Mompha, a ranar Talata.
Kotun ta kuma bukaci mutane biyu da za su tsaya masa, daya daga cikinsu dole ne ya mallaki wata kadara da ta kai Naira miliyan 100 da ke karkashinsa.
Ya mika karar ne ta hannun lauyansa Gboyega Oyewole (SAN).
A baya dai jaridar Dimokuradiyya ta bayar da rahoton cewa hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta sake kama Mompha a ranar 10 ga watan da muke ciki bisa zargin karkatar da kudaden da aka samu ta haramtacciyar hanya da kuma rike kudaden da ake zargin ya aikata.
Shi da kamfanin sa, Ismalob Global Investment Limited, suna fuskantar shari’a kan wasu tuhume-tuhume 22 da aka yi wa kwaskwarima da suka shafi zamba ta yanar gizo da kuma badakalar kudi har Naira biliyan 32.9bn da EFCC ta kawo masa.