By Abbas Yakubu Yaura
A ranar Laraba ne wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin rufe asusun ajiyar banki na gwamnatin jihar Benue bisa zarginta da hannu wajen samun lamuni na Naira miliyan 333 a shekarar 2008.
Alkalin kotun, Inyang Ekwo, ya bayar da wannan umarni ne biyo bayan wani kudiri da hukumar kula da kadarorin Najeriya (AMCON) ta gabatar.
Ya kuma ba da umarnin a dakatar da asusun ajiyar banki na kamfanin HPPS Multilink Services Ltd, har zuwa lokacin da za a ci gaba da sauraren karar.AMCON wanda ita ce mai da’awar, yayin da kamfanin da gwamnatin jihar su ne masu bada amsa na farko da na biyu.
A cikin bayanan, AMCON ta bayyana lamunin a matsayin lamuni mai guba na kadarorin bankin da doka ta mika mata don dawo dasu.”Cewa lamunin ya kasance na tsawon watanni 24 da aka amince da shi bisa ribar kashi 19 cikin 100 a kowace shekara.”
Asusun bankin da abin ya shafa na dukansu na cikin gidane bankin Access, sai Citibank Nigeria Limited, da bankin Eco na najeriya, bankin Fidelity, da bankin First Bank, bankin First City Monument, da bankin GT, sai bankin Heritage, da kuma bankin Keystone.
Kazalika Sauran sun hada da bankin Polaris,da bankin Stanbic IBTC, sai bankin Standard Chartered,bankin Sterling,tare da bankin Suntrust, da bankin Union, bankin United Bank for Africa, da bankin Unity, da bankin Wema, da kuma Zenith.
Comments 1