Wata kotun dake da zama a jihar Neja, ta yankewa wani matashi da yayi luwadi da yaro dan shekaru 12 hukuncin tarar 30,000 da zaman gidan kaso na wata 1 kacal.
Matashin mai suna Abubakar ya turmushe wani yaro mai suna Aminu dan shekara 12 inda ya rinka yi masa lalata har sai da ya ratattaka masa dubura wanda hakan yai sanadiyar rasa ransa.
Al’amarin ya farune a garin kwantagora na jihar Neja.
Gidan Talabijin na NTA a jihar ta bayyana cewa rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar da faruwar al’amarin.
Matashin ya sace yaron ne yakai shi gidan da yake masa luwadin, lamarin daya janyo hankalin makotanshi suka kirawo jami’an ‘yan sanda.
Gidan NTA ya rawaici cewa tuni ‘yan sanda suka kame matashin inda aka garzaya da yaron asibiti domin karbar taimako.
Bayan kaishi asibitin da wasu sa’o’i Aminu yace ga garinku nan.
A bangaren ‘yan sanda kuma, sun gurfanar da matashin a gaban Kotu domin karbar hukunci.
Saidai alkalin ya yankewa Abubakar hukuncin zaman gidan kaso tare da biyan tarar Naira 30,000 kacal.