Daga: Abbas Yakubu Yaura
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi watsi da karar da ke neman a soke rashin cancantar, Adegboyega Oyetola, a matsayin dan takarar Jam’iyyar APC a zaben Gwamnan Jihar da za a yi a ranar 16 ga watan Yuli.
Da yake yanke hukunci, Mai shari’a Inyang Ekwo, ya bayyana cewa mai shigar da kara, Moshood Adeoti, ya gaza tallafa wa tsarin da dokokin da suka dace, don haka bai nuna wani dalili ba a cikin karar da ya sa ya zama babban cin zarafi na tsarin shari’a.
KARANTA WANNAN LABARIN; https://dimokuradiyya.com.ng/kwamishinan-yan-sandan-jihar-adamawa-ya-bada-umarnin-a-mayar-da-lambobin-mota-na-spy/
Mai shari’a Inyang ya kara da cewa karar da aka shigar ta saba wa sashe na 87(9) na dokar zabe da sashe na 22 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya na shekarar 1999 da aka yi wa kwaskwarima.
Adeoti wanda jigo ne a jam’iyyar APC na daya daga cikin ‘yan takara a zaben fidda gwani na gwamna na jam’iyyar APC a jihar a ranar 19 ga watan Fabrairu amma ya rasa tikitin tsayawa takara a hannun gwamna Oyetola.
Daga nan ne ya shigar da karar yana neman a hana gwamnan tsayawa takara saboda rashin cancantar sa ta hannun tawagar lauyoyin sa karkashin jagorancin Babban Lauyan Najeriya (SAN), Chiesonu Okpoko.
A farkon sammacin, ya roki kotu da ta soke takarar Oyetola a kan dalilin da ya sa gwamnan ya yi takara a zaben a matsayin mamba na kwamitin riko na jam’iyyar (CECPC).
Mai shigar da karar ya ce dokar ta ci karo da tanadin sashe na 222 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya na shekarar 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima) da kuma sashi na 31 (iii) na jam’iyyar APC, na watan Oktoban shekarar 2014 (kamar yadda aka yi wa kwaskwarima).
A cewarsa, wanda ake kara na biyu (Oyetola) ya kamata ya yi murabus daga mukaminsa na CECPC a jam’iyyar APC, ya bar ofis a matsayin jami’in APC akalla kwanaki 30 kafin ranar zaben fidda gwani na jihar Osun, domin samun cancantar shiga cikin wannan maganar a zaben fidda gwani na jam’iyyar.
Gwamna Oyetola na neman kara wa’adin mulkinsa na wasu shekaru hudu, bayan ya lashe zaben da ya gabata a shekarar 2018.