Babbar kotun jihar Sakkwato karkashin jagorancin babban Alkali Muhammad Sa’idu Sifawa ta saka ranar 15 ga watan Yuni domin fara sauraren shari’ar ‘yan kasar Chana biyu da hukumar yaki da al’mundahana EFCC ta gurfanar ana zarginsu da bayar da cin hanci.
Voa Hausa sun labarto cewa; EFCC ta gurfanar da mutanen biyu ‘yan asalin kasar Chana gaban kotu ne akan zargin aikata laifuka biyu da suka hada da bayar da toshiyar baki ga jami’in gwamnati da kuma hada baki wajen aikata ba daidai ba.
Mutanen biyu da ake zargin aikata laifukan Meng Kun da Xu Koi, sun ‘ki amincewa da aikata laifukan lokacin da Alkali ya tambaye su. Akan haka ne lauyan masu shigar da kara ya bukaci kotun ta saka ranar da za a fara sauraren karar, inda aka saka ranar 15 ga watan Yuni.